Cikakken tarihin hadiza gabon
SUNA: Hadiza Aliyu Gabon,hadiza gabon
SHEKARU: 1 june 1989
(shekara 32)
AIKI: jaruma, me shirya film
MIJI: babu
YARA: 1 mace
GARI: Kaduna,Libreville
KASA: Nigeria,Gabon
WACECE HADIZA GABON
Hadiza Aliyu wacce akafi Sani da Hadiza Gabon fitacciyar Jaruma kuma me shirya fim a mana’antar kannywood. Hadiza gabon jarumar tana jin yaren harshen Hausa dama turanci. Jarumar tayi jakadanci a kamfanin mtn Nigeria da kamfanin Indomie itace kuma mamallakiyar Hag foundation wadda tabude shine Dan tallafawa marasa karfi.
HAIHUWARTA
An haifi Hadiza Gabon ne a jihar Libreville a kasar Gabon. Mahaifinta Aliyu yakasance dan kasar Gabon ne Mahifiyarta kuma takasance Fulani na jihad Adamawa a Nigeria.
Sannan jarumar tana da yarta daya da ta haifa
KARATUNTA
Jarumar tayi makaranatar primary da makarantar gabada primary a kasar Gabon. Bayan takarasane ta Samu damar shiga jami’a Domin karantun zama alkali, amma bata Samu ta kammalaba saboda wasu dalilai.
daga bisanine ta Shiga makarantar diploma inda takaranci harshen faransanci.
Karanta CIKAKKEN TARIHIN NURA M INUWA
SHIGARTA KANNYWOOD
Hadiza aliyu fara fim nata ya samo asalini tun daga lolacinda taziyarci jihar mahaifiyarta wato jihar Adamawa a nigeria Inda daga bisani ta fara shirya akoma jihad Kaduna domin shiga masana’antar fim na kannywood. sannan Jarumar Ta samu damar ganawa da Ali nuhu inda ta nemi taimakonsa don kaddamar da ita a matsayin yar fim.
Sannan Ta fara fitowa a shirinta na farko tin 2009, a wani fim mai suna Artabu.
Jarumar tasamu nasarar shiga mana’antar kannywood ne da Taimakon jarumi Ali Nuhu dakuma Aminu Sharif wadda akafi sanida Momo.
sannan a shekarar 2017 jarumar ta shiga masana’antar shirya finafinai dake kudancin kasar wato Nollywood wadda tin asali jarumai irinsu Ali Nuhu, Yakubu Mohammed, Sani Danja, Maryam Booth dasauransu suna yin shiri a masana’antar Nollywood, Hadiza Gabon tayi shirinta na farko a masana’antar me suna Lagos Real Fake Life.
A daukita ne a matsayin jaruma yar’wasan kannywood kuma abar koyi musammn yadda take fitowa cikin sutura na al’ada da kyau Hadiza ta kasance itaci jakadiyan da daga cikin camfani sadar wa na najireya mtn da na nigeria da kuma kamfanin abincin indomie, ta karbi kyautar best actress jury award a 2nd kannywood award Wanda kamfanin mtn nigeria suka dauki nauyi bayarwa. itace wadda ta kafa gidauniyar HAG
KYAUTAR KARRAMAWA
A shekarar 2013 tasamu damar zama Gwarzuwar jaruma daga Best of nollywood awards.
A shekarar 2014 tasamu kannywood/MTN award.
An kuma ba ta lambar yabo ta hollwood ta afirka a matsayin jarumar jarumi.
KARIN BAYANI
A 2016, Hadiza Gabon ta kafa kungiyar agaji mai suna hag foundation da nufin ingata rayuwar talakawa ta hanyar Samar da taimako a bangarunri ilimi da kiwao lafiya gami da wadatr da abinci.Ta zama daya daga cikin yan wasa mata na farko a tarihirn kannywood da ta gabatar da irin wannan taimakon na jin kai.
A 2016, ta ziyarci sansanonin yan gudun hijirar dake cikin jihar kano inda ta Ba da gudummawar kayayyakin abnici, da kayain masaka da sauran kayain masarafi da mazauna sansanin suke bukata saboda rikicin arewaci najeriya.
Karanta Cikakken Tarihin Khadija Yobe ( Karima izzarso)
JERIN FINA-FINANTA
-indon kauye
-basaja
-Adnan
-daina kuka
-Farar saka
-Fatakin dare
-Kolo
-Mukaddari
-Sakiyya
-Umarni uwa
-Ziyada
-Hauwa kulu
Dadai sauransu
Sannan takasance daya daga cikin jarumin fimdin gidan badamasi wadda ake haskawa a tashar arewa24
HADAKA
Sannan jarumar tafito a Fina-finai da dama tare da manya da kananun jarumai kamarsu *Ali nuhu *adam a zango *fati washa *mustapha naburaska *horo dan mama *daushe dadai sauransu
Domin Karin bayani dangane da cikakken Tarihin Hadiza Gabon a YouTube Nw Hausa Tv